Isa ga babban shafi
Guinea

Sojojin Guinea sun hana Alpha Conde gudun hijira

Shugabannin sojan Guinea sun ce ba za su bari hambararren shugaban kasar Alpha Conde ya yi  gudun hijira ba, bayan da masu shiga tsakani kungiyar ECOWAS suka yi kokarin matsa lamba don ganin an sake shi.

Kanal Doumbouya, (daga tsakiya) sabon shugaban gwamnatin sojin da suka yi juyin mulki a Guinea, bayan ganawa da tawagar ECOWAS a ranar 10 ga Satumba, 2021 a birnin Conakry.
Kanal Doumbouya, (daga tsakiya) sabon shugaban gwamnatin sojin da suka yi juyin mulki a Guinea, bayan ganawa da tawagar ECOWAS a ranar 10 ga Satumba, 2021 a birnin Conakry. © AP - Sunday Alamba
Talla

Sanarwar gwamnatin sojin ta Guinea a ranar Juma'a ta zo ne bayan kungiyar yankin yammacin Afirka da aka fi sani da ECOWAS ta gana da shugaban ta Kanal Mamady Doumbouya da ya jagoranci juyin mulkin da a farkon wannan wata na Satumba.

Bayan ganawa da Kanal Dambouya, jagoran kungiyar ECOWAS, kuma shugaban kasar Ghana Nana Akufo-Addo, da shugaban Ivory Coast, Alassane Ouattara, sun ziyarci Conde, wanda aka tsare tun lokacin da aka hambarar da shi a ranar 5 ga watan Satumba bayan fiye da shekaru 10 a kan mulki.

A ranar Alhamis, shugabannin kasashen Afrika ta yamma suka kakaba wa jagororin juyin mulkin Guinea takunkumi, kana suka bukaci a gudanar da zabe nan da watanni 6 don maido da mulkin demokaradiyya cikin hanzari a kasar, bayan da sojoji suka hambarar da gwamnatin Alpha Conde  a farkon wannan wata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.