Ana ci gaba da kokarin kashe wutar daji a Algeria
Yanzu haka ana ci gaba da kokarin kashe wutar dajin da ta tashi tun cikin makon jiya a kasar Algeria, inda alkalumma suka tabbatar da mutuwar mutane akalla 90.
Wallafawa ranar:
Minti 1
Talla
Gwamnatin Algeria na binciken musabbabin kashe wani mutun da ake zargi da hannu wajen tashin mahaukaciyar gobarar daji da kasar bata taba ganin irinsa ba.
Bayanai sun ce har zuwa safiyar yau, akwai bakin wuta har guda 19 a wurare daban daban da ake kokarin kashewa a sassan kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu