Isa ga babban shafi
Habasha - Tigray

Habasha ta yi watsi da zargin hana kungiyoyin agaji shiga yankin Tigray

Gwamnatin Habasha ta yi watsi da zargin da ake mata na cewa tana shirin haramtawa kungiyoyin agaji shiga yankin Tigray mai fama da rikici don tallafawa wadanda yaki ya tagayyara.

Wasu mazauna yankin Tigray da rikici ya tilastawa tserewa muhallansu.
Wasu mazauna yankin Tigray da rikici ya tilastawa tserewa muhallansu. AP - Ben Curtis
Talla

Wannan zargi ya bijiro ne kwanaki 2 bayan lalata wasu muhimman gadoji da suke zaman manyan hanyoyin shigar da kayayyakin agaji zuwa yankin na Tigray.

Wasu sojojin 'yan tawayen TPLF mata yayin murnar sake kwace iko da Makele babban birnin yankin Tigray.
Wasu sojojin 'yan tawayen TPLF mata yayin murnar sake kwace iko da Makele babban birnin yankin Tigray. Yasuyoshi Chiba AFP

A makon nan dake shirin karewa ne dai  mayakan ‘yan tawayen TPLF suka yi bazata wajen sake kwace iko da Makele babban birnin yankin, bayan shafe watanni 8 suna gwabza fada sojojin Habasha dake kokarin murkushe su.

Wani rahoton hukumar samar da abinci ta majalisar dinkin duniya WFP, ya ce mutane akalla miliyan 5 da dubu 200 dake zaman kashi 91 cikin 100 na al’ummar yankin Tigray na cikin bukatar agajin gaggawa na kayayyakin abinci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.