Isa ga babban shafi
Gabon

An daure sojojin Gabon da suka yi yunkurin juyin mulki a 2019

An yanke wa sojojin Gabon uku hukuncin daurin shekaru 15 a kidan kaso, sakamakon rawar da suka taka a juyin mulkin da bai yi nasara ba a  shekarar 2019.

Sojojin Gabon lokacin da suka mamaye gidan talabijin kasar a ranar 7 ga watan Janairun 2019.
Sojojin Gabon lokacin da suka mamaye gidan talabijin kasar a ranar 7 ga watan Janairun 2019. AFP - STEEVE JORDAN
Talla

Babban Mai gabatar da karar gwamnatin Gabon wanda ya sanar da hukuncin a wannan Alhamis, yace cikin sojojin ukun, har da Laftanar Kelly Ondo Obiang wanda ke cikin rundunar tsaron fadar shugaban kasa, da ya bayyana a kafar a talabijin din kasar ranar 7 ga watan Janairun shekarar 2019, inda ya yi kira ga jama’a da su fito suyi bore nuna goyan baya ga yunkurin na juyin Mulki.

Sugaban kasar Gabon Ali Bongo, a ranar 16 ga watan Agusta shekarar 2020, yayin jawabi ga 'yan kasa.
Sugaban kasar Gabon Ali Bongo, a ranar 16 ga watan Agusta shekarar 2020, yayin jawabi ga 'yan kasa. Présidence du Gabo
Tun a ranar 18 ga watan Yuni da ya gabata aka fara shari'ar a wata kotun soji ta musamman a Libreville babban birnin kasar, kafin yanke hukuncin cikin daren Laraba.

An wanke mutane shida

Acewar bababn mai gabatar da karar, kotun ta kuma wanke wasu mutane shida da ake tuhuma kan yankurin na hambarar da shugaban kasa Ali Bongo Odimba da baiyi nasaraba, cikinsu harda 'yan sanda biyar da farar hula guda.

Ana ganin hukuncin nada sassauci, domin kuwa tuhuma ne da ya shafi yiwa tsaron kasa zagon kasa, wanda yakan kai ga hukuncin daurin rai-da-rai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.