Isa ga babban shafi
Kenya

Hadarin jirgin Sojin Kenya ya hallaka mutum 10 tare da jikkata 13

Rundunar sojin Kenya ta ce dakarun kasar 10 ne suka rasa rayukansu sanadiyyar hadarin da wani jirgi mai saukar angulu ya yi kusa da birnin da su a safiyar jiya alhamis.

Wani hadarin jirgin sama a Kenya.
Wani hadarin jirgin sama a Kenya. Reuters/Thomas Mukoya
Talla

Sanarwar ta bayyana cewa akwai wasu sojoji 13 da suka samu raunuka a wannan hadari wanda ya faru dai dai lokacin da jirgin ke kokarin sauka.

Ma’aikatar tsaron kasar da ke sanar da faruwar lamarin a safiyar yau, ta ce jirgin Sojin kirar Mi 171 E na dauke da dakarun kasar da ke dawowa daga wani horo na musammanya lokacin da aka samu tangardar sauka da misalin karfe 9 na safiyar jiya.

Sanarwar ma’aikatar da kafofin labaran kasar suka wallafa ta ce za a gudanar da bincike don gano musabbabin faduwar jirgin.

Haka zalika ta sanar da cewa yanzu haka sojoji 13 da suka samu rauni a hadarin na samun kulawar gaggawa a asibitin Soji na birnin Nairobi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.