Mutane 11 sun mutu a rikicin da ya barke akan iyakar Kenya da Somalia
Akalla mutane 11 suka rasa rayukan su sakamakon wani tashin hankalin da aka samu a garin Baled-Hawo a yankin Jubaland dake iyakar Somalia da Kenya, yayin da wasu 11 kumą suka jikkata.
Wallafawa ranar:
Rahotanni sun ce fadan ya barke ne daren ranar lahadi zuwa safiyar litinin, yayin da gwamnatin Somalia ta zargi gwamnatin Kenya da goyawa ‘yan tawaye baya domin kai hare hare a yankin.
Ya zuwa yanzu gwamnatin Kenya bata ce komai ba kan zargin.
Kenya dai ta dade tana goyon bayan Ahmed Madobe shugaban yankin na Jubaland mai kwaryakwaryar ‘yanci, wanda a yanzu dangantaka tayi tsami tsakaninsa da gwamnatin Somalia, abinda ya sanya shi kauracewa zabukan kasar dake shirin gudana.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu