Isa ga babban shafi
Chadi - Rikicin Kabilanci

Rikicin kabilanci ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 100 a Chadi

A kasar Chadi, Kimanin mutane 100 aka kashe a wani rikicin kabilanci a Mouraye Salamat dake kudu maso gabashin ƙasar.

Village sur la route d'Am Timan dans le Salamat, au Tchad.
Village sur la route d'Am Timan dans le Salamat, au Tchad. © wikimedia commons/CC BY-SA 4.0/ Chrisrosenk
Talla

Rikici da Hukumar Kare Hakkin Dan-Adam ta kasa, ta zargi gwamnatin da nuna halin ko-in-kula tare da yin kira da a dauki kwararan matakai don fuskantar abin da ta kira laifukan cin zarafin bil'adama.

Rahotanni suka ce, an dauki tsawon kwanaki, wasu kabilun manoma da makiyaya a kauyukan yankin Mouraye na farmakan juna da kibiyoyi da bindigogi.

Zuwa wayewar safiyar Asabar, yawan mutanen da suka mutu ya haura dari kuma  Shugaban Hukumar Kare Hakkin Dan-Adam ta Kasa, Djidda Oumar, ya daura laifin ga gwamnati.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.