Dimokradiyar Congo na sasanta rikicin Masar da Habasha da kuma Sudan
Ministocin Kasashen Masar da Habasha da Sudan sun fara gudanar da wani taro a Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo da zummar sasanta rikicin da ya biyo bayan shirin gina madatsar ruwan da Habasha keyi akan Kogin Nilu wanda ya haifar da rikici a tsakanin su.
Wallafawa ranar:
Shugaban kasa Felix Tshisekedi dake jagorancin kungiyar kasashen Afirka ta AU ya bukaci ministocin da su bude wani sabuwar kofar da zata bada damar fahimtar juna da kuma kulla yarjejeniya a tsakanin su.
Tshisekedi ya yabawa kasashen uku saboda yadda suka yadda a sasanta barakar dake tsakanin su a Afirka maimakon zuwa kasashen duniya.
Jakadan Amurka a Congo Mike Hammer na daga cikin wadanda suka halarci bikin bude taron.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu