Ta'addanci: Mutane dubu 670 ke gudun hijira a Mozambique
Majalisar Dinkin Duniya tace ‘yan gudun hijira sama da 5 da suka gudu domin tsira da rayukan su daga rikicin da ake yi a garin Palma na kasar Mozambique yanzu haka sun samu mafaka.
Wallafawa ranar:
Mai Magana da yawun hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Sandra Black, ta ce ya zuwa ranar talatar da ta gabata, sun kidaya mutane dubu 5 da 360 da suka isa yankunan Nangade da Mueda da Montepuez da kuma Pemba.
Rahotanni sun ce mutane da dama sun mutu sakamakon hare haren ‘yan tawayen masu ikrarin jihadi.
Rikicin ‘yan bindigar yayi sanadiyar raba mutane kusan 670,000 daga muhallansu a yankin dake da arzikin iskar gas.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu