Isa ga babban shafi
Faransa -Burkina

Dakarun Barkhane sun hallaka 'yan ta'adda 20 a Burkina Faso

Gwamnatin Faransa tace dakarun ta tare da abokan aikin su, sun yi nasarar kashe mahara masu ikirarin jihadi 20 a arewacin Burkina Faso a makon jiya.

Dakarun Faransa na Barkhane dake Mali
Dakarun Faransa na Barkhane dake Mali Daphné BENOIT / AFP
Talla

kakakin sojin kasar Kanar Frederic Barby yace sun samu bayanan asiri ne lokacin da Yan bindigar su kusan 30 ke tafiya akan babura a Boulikessi dake kusa da iyakar Burkina da Mali da Nijar, abında ya sa aka kai musu hari.

Jami’in yace a wannan rana kuma jirgin yakin dake sarrafa kan sa ya kai hari kan motar maharan dake tafiya akan hanyar N’Daki dake cikin Mali.

Kanar Barby yace dakarun rundunar Barkhane tare da masu taimaka musu na cigaba da kai munanan hare hare a yan kwanakin nan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.