Najeriya: 'yan sanda sun tabbatar da sace mutane 6 'yan gida daya a Zamfara
‘Yan sanda a jihar Zamfara dake Najeriya sun tabbatar da sace mutane 6, ‘yayan wani mutum mai suna Sani Gyare da ‘yan bindiga suka yi, da wani karin mutum guda a kauyen Kadauri na karamar hukumar Maru ta jihar.
Wallafawa ranar:
Kakakin rundunar ‘yan sandan, Shehu Mohammed ya tabbatar da aukuwar lamarin ga kamfanin dillancin labaran Najeriya ranar Juma’a a Gusau, in da ya sha alwashin ceto mutanen.
Kamfanin dillancin labaran Najeriya ya ruwaito cewa dimbim ‘yan bindiga ne suka afka wa kauyen da sanyin safiyar Juma’a, inda suka ci Karensu ba babbaka.
Satar mutane don karbar kudin fansa, tare da afka wa kauyuka da makamai ya zama ruwan dare a arewa maso yammacin Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu