Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Jam'iyyar Lumana ta goyi bayan Mahamane Ousmane a zaben Nijar

Wallafawa ranar:

A Jamhuriyar Nijar ,jam’iyyar Lumana ta tsohon Shugaban Majalisar kasar kuma jagoran yan adawa Hama Amadou bayan wani taro da daukacin ya’an jam’iyyar ta bukaci magoya bayan ta da su zabi tsohon Shugaban kasar Mahamane Ousmane a zaben shugabancin kasar na ranar 27 ga watan disambar 2020.

Mahamane Ousmane tsohon Shugaban Jamhuriyar Nijar
Mahamane Ousmane tsohon Shugaban Jamhuriyar Nijar RFI
Talla

A watan Nuwamba ne kotun fasalta kundin Tsarin Mulki a Jamhuriyar Nijar ta yi watsi da takarar Madugun jam’iyyun adawar kasar Hama Amadou dake neman shugabancin kasar.

Da yake yanke hukuncin shugaban kotun fasalta kudin tsarin mulki Bouba Mahamane ya ce, Hama Amadou dake takara karkashin jam’iyyar adawa ta Moden Lumana bai cancanci tsayawa takara ba, saboda hukuncin daurin shekara daya a gidan kaso dake kansa.

Sakamakon rashin tsayawa takarar shugabancin kasa ta madugun yan adawar Nijar Hama Amadou, Jam’iyyarsa ta Lumana ta umurci magoya bayan ta da su jefawa Mahaman Usman na RDR Canji tun zagaye na farko,

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.