Rwanda ta aike da dakarunta Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya
Rwanda ta aike da daruruwan dakarunta zuwa Jamhuriyar Tsakiya Afrika, inda ake kai farmaki kan sojojinta da ke aiki a rundunar kiyaye zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya, kamar yadda ma’aikatar tsaron kasar ta bayyana a wata sanarwa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Sanarwar da ta fito daga ma’aikatar tsaron Rwanda ta ce wannan mataki na zuwa ne a matsayin martani ga hare haren da dakarun ‘yan tawaye masu biyayya da tsohon shugaban kasar Francois Bozize ke kaiwa sojojinta.
A ranar Asabar ne gwamnatin Jamhuriyar Tsakiyar Afrika ta zargi Bozize da kokarin jagorancin juyin mulki, a yayin da hankula ke ci gaba da tashi gabaninn zaben shugaban kasar da zai gudana ranar Lahadi.
Rundunar kiyaye zaman lafiya ta majalisar dinkin Duniya ta ce ‘yan tawaye masu dauke da makamai sun fara kutsawa babban birnin kasar Bangui, amma kuma dakarunta sun maida su baya.
Babu cikakken bayani a kan adadin dakarun da Rwanda za ta tura, ko kuma ran da za ta aike da su, amma ma’aikatar tsaron kasar ta ce za ta kuma taimaka wajen tabbatar da an yi zaben na Lahadi mai zuwa cikin kwanciyar hankali a kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu