Isa ga babban shafi
Somalia

Somalia ta harbe wasu masu wakiltar Al Shebaab wajen aikata kisa

Hukumomin Somalia sun harbe wani malamin makaranta tare da wasu mutane biyu a bainar jama’a saboda samun su da laifin kisa a madadin kungiyar Al Shebaab.

Wasu jami'an Sojin Somalia tare da wasu da ake zargi da aikata laifi a birnin Mogadishu na Somalia.
Wasu jami'an Sojin Somalia tare da wasu da ake zargi da aikata laifi a birnin Mogadishu na Somalia. Reuters
Talla

Malamin Mohammed Haji Ahmed da ke koyar da Turanci a kwalejin Mogadishu na da hannu wajen kashe jami’an gwamnati da dama a madadin kungiyar Al Shebaab.

Rahotanni sun bayyana shi a matsayin mara Imani, wanda ya yi kaurin suna wajen aikata kisan ciki harda na Janar Abdullahi Mohammed Sheikh a shekarar 2017 da mataimakin babban lauyan gwamnati Mohammed Abdurrahman Mohammed a shekarar 2019 da kuma shugaban 'yan Sanda janar Mohammed Haji Alow.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.