Isa ga babban shafi
Afrika

Wakilai 120 daga majalisar Libya suka cimma matsaya A Morocco

Wakilai 120 daga zauren majalisar Libya ne suka cimma matsaya don kawo karshen rikicin kasar a wani taron sassanta shugabanin kungiyoyi dake fada da juna a Libya da ya gudana kasar Morocco.

Taron sassanta yan kasar Libya
Taron sassanta yan kasar Libya Violaine Martin / UNITED NATIONS / AFP
Talla

Kusan shekaru biyu kenan da majalisar ta kasa gudanar da taron ta,tun bayan da Libya ta fada cikin rikici bayan mutuwar tsohon Shugaban ta Mohammar Khadafi a shekara ta 2011.

A watan Oktoba ne aka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin kungiyoyin biyu dake fada da juna a Libya, a wannan karo bayan share kusan kwanaki biyar ana tattauanwa tsakanin bangarorin a Tabger dake Morocco,123 daga cikin wakilai 180 dake zauren majalisa suka amince da rattaba hannu a wannan takardar samar da zaman lafiya da kuma kawo karshen kalaman nuna kyama.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.