Isa ga babban shafi
Habasha - Tigray

Rikicin Habasha: Abiy Ahmed ya yi watsi da kiran kasashe kan yankin Tigray

Firaministan Habasha, Abiy Ahmed ya yi watsi katsalandan din kasashen duniya a harkokin cikin gidan kasarsa, sa’o’i kalilan gabanin cikar wa’adin da ya bai wa jagororin ‘yan tawayen Tigray su mika wuya, ko dandana kudarsu.

Firaministan Habasha Abiy Ahmed.
Firaministan Habasha Abiy Ahmed. REUTERS/Tiksa Negeri
Talla

A Lahadi da ta gabata ne Firaminista Abiy Ahmed, wanda ya lashe kyautar zaman lafiya ta Nobel a bara, ya bai wa ‘yan tawayen kungiyar Tigray People's Liberation Front sa’o’i 72 su mika wuya, amma shugabansu ya yi watsi da kiran, yana mai cewa al’ummar yankin da ke arewacin kasar a shirye suke su sadaukar da rayuwarsu don kare yankinsu.

A yayin da lokacin ke gabatowa, kwamitin tsaro na majalisar dinkin duniya ya gudanar da taronsa na farko a game da rikicin wanda aka shafe makwanni 3 ana yi, inda ya bayyana takaici a game da halin da fararen hula ke ciki a Makele, babban birnin yankin na Tigray.

Yanzu haka dai dakarun Sojin Habasha sun yiwa yankin na Tigray kawanya yayinad suka bukaci ficewar fararen hular da ke zaune a yankin.

Kungiyoyin kare hakkin dan adam sun yi kashedin cewa hari a kan birnin zai zama laifin yaki, suna masu neman gwamnatin Habasha ta yi taka-tsan-tsan, don kaucewar asarar rayuka.

Sai dai Firaminista Abiy Ahmed ya yi watsi da kiran sasantawa, yayinda ya nanata cewa aikin tabbatar da doka a kan kungiyar TPLF ya shiga mataki na karshe.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.