Hukumar zaben Ghana ta hana 'yan takara 5 tsayawa a zaben shugaban kasar mai zuwa
Hukumar zabe a kasar Ghana ta soke takarar mutane 5 dake neman tsayawa a zaben shugaban kasar mai zuwa sakamakon gabatar da takardun bogi.
Wallafawa ranar:
Talla
‘Yan takarar da abin ya shafa sun hada da Kofi Koranteng, dan takarar Indifenda da Marricke Kofi Gane shima daga Indifenda da Akwasi Odike na UPP da Kwasi Busumburu na PAP da Agyenim Boateng na UFP
Hukumar ta kuma ce ta mika sunayen wadannan Yan takara ga rundunar Yan Sanda domin gurfanar da su a gaban shari’a, yayin da zata mayar musu da kudaden takarar da suka gabatar na Cedi 100,000.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu