Isa ga babban shafi
Afrika ta Kudu

Adadin masu Coronavirus a Afrika ta Kudu ya zarce dubu 500

Yanzu adadin wadanda cutar coronavirus ta harba a Afrika ta Kudu ya zarta dubu dari 5, bayan da ma’aikatar lafiyar kasar ta sanar a daren Asabar cewa mutane dubu dari 5 da 3, da dari 2 da 90 ne gwaji ya tabbatar su harbu da cutar.

Shugaban Afrika ta Kudu Cyril Ramaphosa, kasar da annobar corona ta fi kamari a Afrika.
Shugaban Afrika ta Kudu Cyril Ramaphosa, kasar da annobar corona ta fi kamari a Afrika. PHILL MAGAKOE / AFP
Talla

Wannan ya dora kasar a matsayin inda wannan cuta ta fi yin ta’adi, inda fiye da rabin wadanda cutar ta kama a nahiyar Afrika a cikinta suke.

Ya zuwa yanzu, mutane dubu 8 da dai da 53 ne cutar ta kashe, sai dai masu bincike na cikin gida na cewa adadin na iya zarce haka.

Afrika ta Kudu na daga cikin kasashen da ke da bangaren lafiya maai inganci a nahiyar Afrika, ama kuma duk da haka sai da wannan cuta ta buwaye ta sakamakon rashawa da samar da kayayyakin kariya ga ma’aikatan lafiya a asibitocin gwamnati.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.