Za'a rantsar da sabon shugaban kasar Burundi bayan mutuwar Nkurunziza
Gwamnatin Burundi ta ce a ranar Alhamis mai zuwa za’a rantsar da zababben shugaban kasa Evariste Ndashimiye kamar yadda kotun koli ta bada umurni domin maye gurbin shugaba Pierre Nkurinziza da ya mutu a makon jiya.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Tuni ma’aikatar harkokin wajen kasar ta aike da takardun gayyata ga jakadu da jami’an diflomasiya domin halartar bikin shan rantsuwar da za’ayi a Gitega, babban birnin kasar.
Ndashimiye mai shekaru 52, tsohon Janar ne na sojin kasar kana kuma tsohon dan tawaye ne daga bangaren Yan kabilar Hutu a rikicin kasar.
A zaben da ya gudana, Ndashimiye ya samu kusan kashi 69 na kuri’un da aka kada, abinda ya bashi nasara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu