Isa ga babban shafi
Coronavirus

Mai yiwuwa kasashen Turai su yafe bashin da suke bin yankin Sahel

Kasashen dake kungiyar tarayyar Turai EU, sun ce zasu tattauna bukatar yafewa kasashen Sahel bashin da suka gabatar, bayan tattaunawar da aka yi ta bidiyo tsakanin shugabannin kasashen yankin da kuma shugaban majalisar Turai Charles Michel.

Shugaban Majalisar Turai Charles Michel.
Shugaban Majalisar Turai Charles Michel. REUTERS/Francois Lenoir
Talla

Michel yace kasashen Sahel da suka hada da Mauritania, Mali, Burkina Faso, Nijar da kuma Chadi na fuskantar yaki da yan ta’adda a kusan shekaru 8 da suka gabata.

Jami’in yace bayan tattaunawar da suka yi a tsakanin su, yanzu sun amince su gudanar da taro akai tare da abokan huldar su irin su hukumar IMF domin daukar matsayi akai.

Kasashen duniya na kallon nahiyar Afirka a matsayin yankin da annobar coronavirus za tayi matukar illa saboda rashin harkokin kula da lafiya masu inganci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.