An kama wasu yan kasar Belgium a Cote D'Ivoire
Hukumomin kasar Belgium sun sanar da kama wasu mutane biyu da aka bayyana su cikin jerin mutanen da aka fi nema a Turai, saboda zargin kisan gillar da ake musu na kashe wani Dan kasar Birtaniya a shekarar 1996.
Wallafawa ranar:
Tareda hadin gwiwar yan Sandar kasar Cote D’Ivoire da hukumar yan Sanda ta kasa da kasa ,Interpol ne aka samu nasarar cafke mutanen biyu a Abidjan.
An kama mutanen biyu Hilde Van Acker da Jean Claude Lacote ne a Abidjan dake Cote d’Ivoire bayan kwashe shekaru 20 ana neman su.
Ana zargin mutanen biyu ne da harbe Marcus John Mitchell a kai a gabar teku, inda daga bisani suka yi batar dabo.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu