Harin nakiya ya hallaka mutane 5 a Burkina Faso
Mutane biyar, hudu daga cikinsu jami’an ‘yan sanda sun hallaka a Burkina Faso, lokacin da motarsu ta taka wata nakiya da aka binne.
Wallafawa ranar:
Harin ya auku ne a garin Boungou dake gabashin kasar, inda a baya bayan nan ake fuskantar karuwar hare-hare daga kungiyoyi masu da’awar jihadi.
Tawagar jami’an tsaron na kan aikin rakiyar wasu ma’aikatan hakar ma’adanai ne a lokacin da suka gamu da ajalin nasu.
Ko a watan Agutan da ya gabata akalla mutane 6 ne suka hallaka a makamancin harin na jiya, wanda ya kawo yawan jami’an tsaron Burkina Faso da suka hallaka a hare-haren zuwa 40, daga watan Augutan zuwa yanzu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu