Sojan Mali na da hannu a kisan mutane a garin Mopti
Ministan tsaron Mali ya ce binciken farko da aka gudanar, na tabbatar da cewa sojojin kasar na da hannu wajen kisan mutane 25 da aka gano kaburburansu a yankin Mopti da ke tsakiyar kasar.
Wallafawa ranar:
Gwamnatin Mali ta aike da tawaga da ta je domin binciken,
Tawagar kwararri, wadda ta gano cewa lalle akwai mutanen da aka kashe sannan kuma sojoji na da hannu a lamarin,
Bayan gabatar da wannan rahoto, mataki na farko da hukuma ta dauka shi ne bai wa babban kwamandan askarawan kasa umarnin kai ziyara a yankin domin duba irin matakan da ya kamata a dauka a bangaren soji musamman hukunta wadanda ke da hannu a lamari.
Wannan na nufin cewa duk wanda aka tabbatar da cewa yana da hannu a lamarin zai fuskanci hukunci kamar yadda ka’idar aikin soji ta tanada, sannan kuma ya fuskanci hukunci na shara’a.
Minista Tiena Coulibaly ya ce ko shakka babu za a hukunta wadanda aka sama da laifi wajen aikata wannan kisa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu