Isa ga babban shafi
Mali

Yan bindiga sun kashe dakarun Majalisar Dinkin Duniya a Kidal

Majalisar Dinkin Duniya ta ce an kashe dakarun ta guda biyu dake aikin samar da zaman lafiya a Mali, yayin da aka raunana wasu guda 10 a harin da aka kai sansanin su dake Aguelhok.

Aguelhok dake arewacin garin Kidal yankin da aka jibge dakarun Minusma
Aguelhok dake arewacin garin Kidal yankin da aka jibge dakarun Minusma David Baché/RFI
Talla

Kungiyar MINUSMA dake kula da dakarun, ta ce an kai harin ne da misalin karfe 6 da mituna45 na yammacin jiya juma’a, lokacin da aka harba musu makami mai linzami.

Ya zuwa yanzu ba’a iya tantance ko sojojin wacce kasa ne hadari ya ritsa da su ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.