Tsarin fasalta siyasar Afrika ta bangaren tsaro da yaki da cin hanci
Yau litinin Shugabannin kasashen Afirka ke ci gaba da taron su a Addis Ababa, inda ake saran zasu mayar da hankali kan shirin yaki da cin hanci da rashawa.Tuni kungiyar ta bayyana nada shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari a matsayin wanda zai jagoranci yakin, kuma shi ake saran ya jagoranci zaman taron na yau.
Wallafawa ranar:
Kunna - 00:58
A daya bangaren Sakatary Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya bayyana damuwar sa gani kalubale da dakarun wanzar da zaman lahiya ke fuskanta a Nahiyar Afrika wajen gudanar da ayyukan su.
Guterres ya bukaci kasashen Afrika su bayar da hadin kai a kokarin su na yakar kungiyoyin dake dauke da makamai. Lamarin dake kawo koma baya ga kokarin majalisar Dinkin Duniya na wanzar da zaman lahiya a yankin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu