Isa ga babban shafi
Congo

Jami'an tsaro na kashe masu zanga-zanga a Congo

Mutane 8 aka kashe yayin da aka raunata sama da 100 a zanga-zangar da ake yi na neman shugaban ƙasar Congo Joseph Kabila da ya sauka daga kan mulki.

Masu zanga-zangar neman shugaban Congo Joseph Kabila ya sauka daga muliki a Kinshasa.
Masu zanga-zangar neman shugaban Congo Joseph Kabila ya sauka daga muliki a Kinshasa. John WESSELS / AFP
Talla

Akasarin masu zanga-zangar kiristoci ne mabiya ɗariƙar katolika waɗanda suka taru a majami’u da ke faɗin ƙasar domin gangamin neman shugaban ya kauce daga mulki.

Wakilin kamfanin dillancin labaru na Faransa ya ce, ya gani da idonsa yadda sojoji suka harbi wani mutum a ƙirji lokacin da suka bude wuta a kan masu zanga-zanga.

A wani yanki na Kinshasa babban birnin ƙasar, an yi amfani da barkono mai sa hawaye domin tarwatsa mutane, sannan aka damƙe masu jagorantar zanga-zangar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.