Isa ga babban shafi
KENYA

Hukumar zaben Kenya ta sallami manyan jami'anta.

Hukumar zaben Kenya ta sauke wasu daga cikin manyan jami’anta 7 daga bakin aiki, tare da maye gurbinsu da wasu daban. Matakin dai na zuwa ne bayan sharuddan da jagoran adawa Raila Odinga ya gindaya kafin amincewa ya sake fitowa a zaben kasar na watan Oktoba da kotu ta sanya.

Dandazon magoya bayan jagoran Adawa na Kenya Raila Odinga ke nuna farin cikinsu baya da kotun kolin kasar ta ta zartas da hukuncin rushe zaben kasar na watan Agusta da ya bai wa Uhuru Kenyatta nasara.
Dandazon magoya bayan jagoran Adawa na Kenya Raila Odinga ke nuna farin cikinsu baya da kotun kolin kasar ta ta zartas da hukuncin rushe zaben kasar na watan Agusta da ya bai wa Uhuru Kenyatta nasara. Reuters
Talla

Hukumar zaben ta sauya Daraktan fasahar sadarwa na ICT James Muhati da Albert Gogo, sai kuma Mr Marjan Hussein Marjan daraktan kula da shirye-shiryen hukumar yayinda Dr Sidney Namulungu zai jagoranci bangaren gudanarwa.

Sauran sun hada da Ms Nancy Kariui a matsayin shugabar sashen samar da kayayyakin zabe da kuma Mr Bernard Misati Moseti a matsayin shugabar sashen bayar da horo na hukumar.

A cewar shugaban hukumar Mr Chebukati, dukkanin nade naden za su fara aiki nan ta ke har zuwa watanni uku masu zuwa bayan kammala zaben kasar da kotu ta sanya ya gudana cikin watan Oktoba mai zuwa.

Matakin sauya manyan jami’an hukumar zaben dai na zuwa ne kwanaki kadan bayan Jagoran adawa Raila Odinga ya gindaya sharuddan cewa ba zai shigo a dama da shi a zaben kasar ba, matukar ba a sauya wasu daga cikin jami’an hukumar ba.

Matakin da a baya wasu ke kallo a matsayin abin da ba zai yiwu ba, la'akari da cewa dukkanin jami'an hukumar gwamnati mai ci ta Uhuru Kenyatta ce ta nada su kan mukaman da su ke.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.