Isa ga babban shafi
Afrika ta Tsakiya

Human Rights Watch ta zargi sojojin Uganda da ci zarafin mata

Kungiyar Agaji ta Human Rights Watch ta yi zargin cewar sojojin kasar Uganda dake aikin samar da zaman lafiya a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya da kuma ke farautar shugaban Yan Tawaye Joseph Kony sun ci zarafin mata da 'Yan mata 13.

Wasu daga cikin 'yan gudun hijira  da rikicin kasar ya raba da muhallansu
Wasu daga cikin 'yan gudun hijira da rikicin kasar ya raba da muhallansu REUTERS/James Akena
Talla

Kungiyar ta ce ta samu hira da mata sama da dozen guda da suka yi wannan zargi cewar sojojin sai sun yi lalata da su kafin su basu abinda zasu ci, kuma sun tabbatar da aukuwar lamarin.
Wasu daga cikin Yan matan sun ce yanzu haka suna dauke da juna biyu sakamakon cin zarafin.

Richard Karemire, mai Magana da yawun sojin Uganda ya ce suna gudanar da bincike a kai.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.