Isa ga babban shafi
Sudan ta Kudu

Rikici ya sake barkewa a Sudan ta Kudu

Rahotanni daga Sudan ta Kudu sun ce, an samu barkewar tashin hankali a Malakal, birni na biyu mafi girma a kasar kuma cibiyar hakar man fetur.

Rikici ya sake barkewa a yankin Malakal na Sudan ta Kudu
Rikici ya sake barkewa a yankin Malakal na Sudan ta Kudu REUTERS/Jok Solomon
Talla

Kakakin sojin Sudan ta Kudu, Kanar Santo Domic Chol ya ce, 'yan tawayen sun dade suna neman tada hankali bayan zaman lafiyar da aka samu a yankin.

Sai dai kakakin 'yan tawayen Gatjiath Deng, ya zargi sojojin ne da kaddamar da hari a sansaninsu.

Deng ya ce, dakarun sun yi nasarar kassara sojojin gwamnati a karawar da aka yi.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.