Dangote ya sake rufe kamfanin sarrafa tumatur a Lagos
Attajirin Afrika Alhaji Aliko Dangote ya sake rufe kamfaninsa na sarrafa tumatur a Lagos kudancin Najeriya bayan ya rufe na Kano a arewacin kasar. Dangote ya rufe kamfanin ne saboda karancin dalar Amurka da za a shigo da kayayyakin aikin sarrafa tumaturin.
Wallafawa ranar:
Wannan kuma koma-baya ne ga gwamnatin Muhammadu Buhari da ke kokarin karkatar da tattalin arzikin Najeriya daga dogaro da arzikin fetir.
A taron tattalin arziki da ake gudanarwa a Davos, Mataimakin shugaban Najeriya Yemi Osinbajo ya ce za su yi kokarin magance wagegen gibin da ake samu a kasuwar canji tsakanin farashin gwamnati da na kasuwar bayan fage.
Tsadar Dala da karancinta ya kuma sa Dangote ya dakatar da wasu kasuwancinsa na kayayyakin abinci da suka shafi Suga da fulawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu