Isa ga babban shafi
Nigeria

Kamfanin Dangote na shirin gina matatar mai da kamfanin sarrafa taki

Shugaban Kamfanin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ya sanar da shirin gina katafariyar matatar man fetur a Najeriya, tare da kamfanin yin takin zamani wanda zai ci kudi Dala biliyan 9, don rage dogaron shigar da tacaccen mai a kasar.

Aliku Dangote
Aliku Dangote
Talla

Sanarwar da kamfanin ya bayar, ta nuna cewar, kamfanin ya kulla yarjejeniya da wasu bankuna na samun rancen Dala biliyan kusan uku da rabi na gina matatar man, wadda ake saran zai samar da ayyukan yi 9,500 da kuma samar wa ‘yan kasuwa sama da 25,000 abinda za su yi.

Ana saran kammala gina matatar a kudu maso Yammacin Nigeria cikin shekaru 3 zuwa 4.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.