Isa ga babban shafi
DR Congo

Rikicin kabilanci a Jamhuriyar Congo ya hallaka mutane 34

Wata kungiyar ‘yan ta’adda daga kabilar Nande ta kashe fararen hula 34 ‘yan kabilar Hutu a wani tashin hankali a tsakanin bangarorin biyu a Jamhuriyar Demokradiyyar Congo.

Rikicin kabilanci na kara tsananta a Congo.
Rikicin kabilanci na kara tsananta a Congo. AFP/Adia Tshipuku
Talla

Shugaban mulkin Yankin Lubero dake Arewacin Kivu, Joy Bokole ya ce maharan sun kai samamen ne a kauyen Luhanga jiya da asuba dauke da bindigogi da kuma adduna.

Rikicin kabilanci da kuma kokarin mallakar ma’adinai na daga cikin abinda ke raba kan kabilun kasar wadanda ke fada da muggan makamai.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.