Nijar
Amurka ta horar da 'Yan Sandan Nijar 250 dan yaki da Boko Haram
Sojojin Kasar Amurka sun horar da ‘Yan Sandan Nijar 250 dan yaki da kungiyar Boko Haram a Jihar Diffa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Talla
Yayin bikin yaye ‘Yan Sandan, Idder Adamu, babban magatakardan ofishin ministan cikin gidan Nijar ya ce Nijar ta bukaci horo ne daga Amurka saboda karfin da ta ke da ita.
Idder ya kuma bayyana ya cewa sun samu kayan aiki baya ga horo da suka samu daga Sojin, tare da jadadda nasaran da suke samu a yaki da ta’addanci.
Hare-hare Boko Haram ya salwantar da rayuka tare da raba daruruwa da gidajensu a yankin Diffa da ke iyaka da Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu