Sabon Mataimakin Shugaban Sudan ta Kudu na ziyarar a Khartoum
Sabon mataimakin shugaban kasar Sudan ta Kudu Taban Deng Gain na shirin tafiya kasar Sudan gobe lahadi domin ziyara ta kwanaki biyu inda ake sa ran ya tattauna batutuwa da dama da jami'an Khartoum.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Ziyarar tasa ita ce ta farko tun bayan hawansa kujeran mataimakin shugaban Sudan ta Kudu.
Jakadan Sudan ta kudu a Khartoum, Mayan Dout ya shaidawa kamfanin Dillancin labaran Faransa AFP cewa wasu ministoci da mashawartan Shugaba Salva Kiir zasu rufa masa baya a tattaunawan irin sa na farko don warware wasu batutuwa da ba'a warware ba tun bayan samun 'yanci..
Gwamnatin Salva Kiir har yanzu bata ce ga inda tsohon mataimakin shugaban kasar Reik Machal yake ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu