Tarzoma na kara tashi a Zambia gabanin Babban zaben ranar Alhamis
Magoya bayan ‘yan takaran shugabancin kasar Zambia a zaben Alhamis dake tafe na gwabza fada da juna al’amarin da ke haifar da fargaba gameda dorewar zaman lafiya a wannan kasa da ba’a santa da munanan rikici ba.
Wallafawa ranar:
Ranar Alhamis ne Shugaban kasar Edgar Lungu zai kara da abokin adawar sa Makainde Hichilema, a zaben da ‘yan takara shugabancin kasar tara ke fafatawa.
Magoya bayan ‘yan takaran shugabancin kasar musamman na shugaba mai ci da babban abokin adawar tasa sun fi samun rikici tsakanin su.
Ranar littini an sami yamutsi tsakanin magoya bayan jamiyyar Shugaban kasar da kuma na jagoran adawa Makainde Hichilema.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu