Isa ga babban shafi
Afrika

An tarwatsa 'yan adawa a Zimbabwe

‘Yan sanda a Zimbabwe sun tarwatsa wata zanga-zangar da masu adawa da shugabancin Robert Mugabe suka gudanar yau laraba a birnin Harare.

Shugaban Zimbabwe Robert Mugabe
Shugaban Zimbabwe Robert Mugabe WILFRED KAJESE / AFP
Talla

‘Yan sanda sun yi amfani da motocin ruwan zafi, kulake da kuma hayaki mai sa kwalla domin tarwatsa daruruwan ‘yan adawar da suka taru a gaban ginin ma’aikatar kudin kasar.

A shekara ta 2009 ne gwamnatin kasar Zimbabwe ta dauki matakin daina amfani da takardar kudinta saboda matsalar hauhawar farashin kayayyaki da faduwar darajar kudin inda ta dogara kan dala.

Shugaban kasar Zimbabwe Robert Mugabe mai shekaru 92 wanda ke rike madafun ikon kasar tun bayan samun ‘yancinta daga Birtaniya a 1980 na fuskantar matsin lamba daga ‘yan adawar kasar na ya sauka daga mukaminsa.

 

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.