An kashe ‘Yan Boko Haram 15 a harin sama
Rundunar Sojin saman Najeriya ta sanar da kai harin bam kan tawagar kungiyar Boko Haram a arewacin jihar Barno wanda ya kashe 15 daga cikinsu tare da jikkata wasu da dama.
Wallafawa ranar:
Kakakin sojin saman Ayodele Famuyiwa ya ce jiragen yakin sama a karkashin ‘Operation Gama Aiki’ da aka kaddamar a makon jiya ne suka kai harin kan mayakan kungiyar da ke tserewa daga Dajin Sambisa.
Sannan harin ya jikkata wasu da dama, bayan kashe 15 daga cikin su.
Rundunar sojin kasa da ke fada da ‘Yan Boko Haram a yankin ta tabbatar da adadin mutanen 15 da aka kashe.
A ranar Juma’a ne 19 ga watan Yuni aka kaddamar da jiragen yakin domin yakar Boko Haram.
NAF ALPHA JET FOILS PLAN TO AMBUSH SURFACE FORCES, KILLS 15 BOKO HARAM TERRORISTShttps://t.co/CrC6TklxMT pic.twitter.com/bTRGmorDn0
— Nigerian Air Force (@NigAirForce) June 19, 2016
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu