Isa ga babban shafi
Sudan ta Kudu

Akalla mutane dubu 50 sun mutu a yakin Sudan ta Kudu

Majalisar dinkin duniya ta bayyana cewa, akalla mutane dubu 50 ne suka rasa rayukansu a yakin basasar Sudan ta Kudu, adadin da ya ninka wanda kungiyoyin agaji suka bayar sau biyar.

Majalisar dinkin duniya ta ce,  yakin Sudan ta Kudu ya kashe mutane akalla dubu 50 tare da tilasta wa sama da miliyan 2 kaurace wa gidajensu.
Majalisar dinkin duniya ta ce, yakin Sudan ta Kudu ya kashe mutane akalla dubu 50 tare da tilasta wa sama da miliyan 2 kaurace wa gidajensu. Justin LYNCH / AFP
Talla

Rikicin siyasa tsakanin shugaban kasar Salva Kiir da kuma tsohon mataimakinsa, Riek Machar, shi ne musabbabin barkewar yakin a watan Disamban shekara ta 2013.

Wani babban jami’in majalisar dinkin duniya ya shaida wa manema labarrai cewa, yakin ya haifar da ‘yan gudun hijira sama da miliyan 2 .

Sannan ya bayyana shakkunsa game da yiwuwar aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiyar kasar da aka kulla a watan Agustan da ya gabata.

A watan jiya ne majalisar dinkin duniya ta ce, bangarorin da ke fada da juna a Sudan ta Kudu na kashe mutane tare da lalata kayayyakinsu duk da yarjejeniyar da Kiir da Machar suka rattaba wa hannu.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.