Isa ga babban shafi
Nijar

CENI ta yi watsi da zargin ‘Yan adawar Nijar

Hukumar zaben kasar Nijar mai zaman kanta CENI, ta yi watsi da zargin ‘yan adawa da suka ce ba za su amince da sakamakon zaben shugaban kasa saboda an yi magudi.

Boube Ibrahim, Shugaban hukumar Zaben Nijar
Boube Ibrahim, Shugaban hukumar Zaben Nijar CENI-NIGER
Talla

Kawo yanzu hukumar zabe ta fitar da sakamakon zaben shugabancin kasa na kananan hukumomi 86 daga cikin 308, da aka gudanar a ranakun Lahadi da Litinin.

Sai dai hudu daga cikin ‘yan takarar daga bangaren adawa sun ce ba su amincewa da sakamakon bisa zargin yin magudi.

a tsarin dokar zaben Nijar dai kwanaki biyar aka kayyade domin bayyana kammalallen sakamkon zaben shugaban kasa da na ‘Yan Majalisu.

‘Yan takara 14 ne suka fafata da Shugaba mai ci Mahamadou Issoufou na Jam’iyyar PNDS Tarayya kuma alamu na tabbatar da cewa shi zai lashe zaben tun a zagaye na farko.

01:33

CENI ta yi watsi da zargin 'Yan adawar Nijar

Lydia Ado

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.