Isa ga babban shafi
Egypt

Shugabannin kasashen Africa na taro a Masar game da bunkasa tattalin arziki

Shugaban kasar Masar Abdel Fattah al-sisi yau asabar ya bude wani babban taron bunkasa tattalin arzikin kasashen Africa, dake samun halarcin shugabannin kasashen Africa da wasu fitattun ‘yan kasuwa na nahiyar. 

Shugaban Masar  Abdel Fattah al-Sisi yana jawabi a wani taro.
Shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi yana jawabi a wani taro. REUTERS/The Egyptian Presidency/Handout via Reuters.
Talla

Taron wanda aka saba yi na kwanaki biyu a wajen shakatawa na  Sharm-el Sheikh na samun halarcin wakilai dubu da dari biyu.

Masana kan rika cewa duk da bunkasar da nahiyar Africa ta yi, harkokin ciiniki da kasuwancin nahiyar bai wuce kashi biyu daga cikin dari ba na harkokin ciniki da kasuwanci na duniya.

Shugabannin kasashen da suka halarci taron sun nemi masu zuba jari da su zuba jarin su wajen habaka nahiyar ba tare da fargaban halin ta'addanci da wasu kasashen nahiyar ke fama dashi ba.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.