Buhari ya aike da tawaga Dalori
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya aika da wata tawagar gwamnati zuwa garin Dalori cikin jihar Borno inda mayakan Boko Haram suka kashe mutane sama da 80 tare da kona gidaje.
Wallafawa ranar:
Maitamakin gwamna Borno ne ya tarbi tawagar karkashin jagorancin Sakataren gwamnatin Tarayya David Lawal zuwa Dalori domin jajantawa mutanen garin da kuma ganin irin girman barna da Boko Haram ta aikata domin daukar matakin da ya dace na tallafawa mutanen garin.
Gwamnati Najeriya na ci gaba da bayana fatan ta na kawo karshan ayyukan Boko Haram a arewacin kasar, to sai dai mayakan na sake kaddamar da sabbin hare-hare a kasar dama makabciyarta Kamaru.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu