Isa ga babban shafi
Afrika taTsakiya ,AU

YanTawayen Afrika ta Tsakiya sun kafa yanki mai cin gashin kan sa

Shugaban ‘yan tawayen Seleka na jamhuriyar Afrika ta tsakiya, Noureddine Adam ya sanar da kafa yanki mai cin gashin kan sa a arewa maso gabashin kasar, a dai dai lokacin da ake shirin gudanar da zabe a ranar 27 ga watan disemba.

Wasu yan kungiyar  Seleka a Birni Bambari dake Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya
Wasu yan kungiyar Seleka a Birni Bambari dake Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya REUTERS/Goran Tomasevic
Talla

Mai Magana da yahu shugaban ‘yan tawayen Seleka, Maouloud Moussa ya ce, a jiya litinin ne suka ayyana yankin Logone da ke garin Kaga-Bandoro a matsayin jamhuriya mai cin gashin kai.

Shugaban ‘yan tawayen Seleka dai ya yi watsi da shirin zaben kasar wanda ake fatan zai kawo zaman lafiya a Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya.
  Jamhuriyar Afrka ta Tsakiya  na daga  cikin kasashen  Afrika da talauci ya yiwa kanta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.