Isa ga babban shafi
Kamaru

An kai harin kunar bakin wake a Kamaru

Hukumomin tsaro na kasar Kamaru sun bayyana cewa wasu mutane da ake zaton mayakan Boko Haram ne sun kaddamar da hare haren kunar bakin wake a yankin arewacin kasar, inda akalla mutane uku suka rasa rayukansu.

Boko Haram ta sha kai hare hare a kasar Kamaru.
Boko Haram ta sha kai hare hare a kasar Kamaru.
Talla

An kaddamar da jerin hare haren ne guda biyu a cikin daren jiya a Waza da ke yankin arewa mai nisa yayin da wasu rahotannin ke cewa adadin wadanda suka rasu ya kai shida.

A bangare guda, jami’an tsaro sun yi nasarar hallaka wata ‘yar kunar bakin waken dabam da ta yi yunkurin tayar da bam din da ke jikinta.

Kungiyar Boko Haram dai ta sha tura ‘yan mata domin kaddamar da harin kunar bakin wake a Kamaru kuma al-amarin na neman zama ruwan dare.

Kasar Kamaru na cikin kasashen yankin tafkin Chadi da ke kokarin kawo karshen kungiyar Boko Haram wadda ta hallaka mutane da dama.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.