Somalia
Mutane 12 sun mutu sakamakon harin Alshabab a Mogadishiu
Hukumomi a kasar Somalia sun tabbatar da mutuwar mutane 12, sakamakon harin da ‘yan bindiga suka kai a wani hotel da ‘yan majalisar dokokin kasar ke zaune a birnin Mogadishiu.
Wallafawa ranar:
Talla
Majiyoyin ‘yan sanda sun ce a sanyin safiyar yau ne ‘yan bindigar suka afka wa wannan hotel, yayin da wasu majiyoyi ke cewa da farko wata mota ce da aka dana bam ta tashi a harabar wannan hotel kafin a fara buda wuta.
Tuni dai jami'an wanzar da tsaro da zaman lafiya na Tarayyar Afirka suka kwace iko da wannan otel.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu