Isa ga babban shafi
Libya

Kwamandojin 'yan tawaye sun mutu a hatsarin jirgin saman Libya

Wani jirgi mai saukar angulu dauke da mutane 23 ya fado a kusa da birnin Tripoli na kasar Libya to sai dai kawo yanzu babu cikakkun bayanai a game da dalilan wannan hatsari.

Znga-zanga a birin Benghazi na Libya
Znga-zanga a birin Benghazi na Libya REUTERS/Esam Omran Al-Fetori
Talla

Kawo yanzu an tabbatar da mutuwar mutane 9, yayin da bayanai ke nuni da cewa da dama daga cikin wadanda ke cikin jirgin manyan kwamandojin ‘yan tawayen da ke mamaye da birnin Tripoli ne.

Libya dai kasa ce da ke fama da rikici tun a shekara ta 2011 lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar shugaban kasar Mu’ammar Kaddafi, kuma tun a wannan lokaci ba wata karbabbiyar gwamnati a kasar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.