Isa ga babban shafi
Afrika

Bankin raya Afrika zai mayar da hankali ga samar da Lantarki

Sabon shugaban Bankin raya Afrika AFDB, ya ce a shekaru masu zuwa nan gaba, Bankin zai mayar da hankali ne wajen magance matsalar karancin wutar lantarki domin bunkasa tattalin arzikin kasashen Afrika.

Sabon Shugaban Bankin raya Afrika Akinwumi Adesina Dan Najeriya
Sabon Shugaban Bankin raya Afrika Akinwumi Adesina Dan Najeriya AFP PHOTO/ SIA KAMBOU
Talla

Matsalar lantarki dai na durkusan da masana’antu a Afrika, al’amarin da ke gurgunta tattalin arzikin kasar, a cewar Akinwumi Adesina.

Ya kara da cewa matsalar na haifar da rashin ayyukan yi ga matasa.

Wasu alkalumma na hukumar makamashi ta duniya sun bayyana cewa Afrika na bukatar kudi da suka kai dala biliyan 450 domin bunkasa lantarki a birane daga nan zuwa shekarar 2040.

Sabon shugaban ya ce magance matsalar makamashi shi ne babban abin da zai sa gaba, kamar yadda ya shaidawa kamfanin dillacin labarain Reuters, a Abidjan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.