Isa ga babban shafi
Libya-Al Qaeda

Al Qaeda ta karyata labarin mutuwar Belmokhtar

Kungiyar Al-Qaeda a reshen arewacin Afrika ta karyata rahotannin da ke cewa hare haren da Amurka ta kai kasar Libya a makon da ya gabata, sun hallaka tsohon shugabanta Mokhtar Belmokhtar, kamar yadda kungiyar ta sanar.

Mokhtar Belmokhtar, Kwamandan Al Qaeda
Mokhtar Belmokhtar, Kwamandan Al Qaeda REUTERS/Belmokhtar Brigade/Handout
Talla

Cikin Sanrwar da ta sanya a shafin Internet a wayewar garin yau Juma’a, kungiyar ta ce mujahid Khaled Abu al-Abbas kamar yadda ake kiransa Belmokhtar, yana nan cikin koshin lafiya.
A ranar Lahadi hukumomin kasar Libya suka fitar da sanarwar mutuwar Belmokhtar, wanda aka dade ana bayar da sanarwa mutuwar shi.

Bangaren mayakan Ansar al Shari’a a Libya da ke da alaka da Al Qaeda sun karyata labarin kisan Belmoktar.

Amurka dai tace ta yi ruwan bama bamai da jiragen sama a inda Belmokhtar ke buya amma ba tare da ikirarin ta kashe kwamandan ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.