Burundi-Election
An dage zaben Burundi
Hukumar zaben kasar Burundi ta sanar da dage zaben shugaban kasar zuwa ranar 15 ga watan Yuli mai zuwa, bayan an kwashe makwanni ana ta zanga zangar adawa da takarar shugaba Pierre Nkurunziza na wa’adi na uku.
Wallafawa ranar:
Talla
Shugaban hukumar Pierre Clever Ndayicariye ya sanar da haka kamar yadda shugabanin kasashen dake Gabashin Afrika suka bada shawara.
Ya zuwa yanzu dai kusan mutane 40 aka tabatar da mutuwar su a rikicin siyasar kasar Burundi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu