Sojoji sun kwace mulki a Burundi
Tsohon Babban hafsan Sojan Burundi Janar Godefroid Niyombare ya sanar da hambarar da gwamnatin Pierre Nkurunziza, bayan shafe makwanni ana zanga-zangar adawa da matakinsa na yin tazarce.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Janar Niyombare ya sanar da hambarar da gwamnatin Nkurunziza a kafar yada labaran kasar.
Janar Niyombare ya taba rike mukamin babban hafsan Soji, kafin a tube shi a watan Fabrairu, kuma ya kwace mulki ne bayan Nkurunziza ya kama hanya zuwa taron kasashen gabacin Afrika a Tanzania game da rikicin kasar.
Niyombare ya bukaci al’ummar Burundi su kare rayuka da dukiyoyin Jama’a.
A yau Laraba ne Shugabannin kasashen gabacin Afrika za su gudanar da taro a Tanzania domin tattauna rikicin Burundi inda aka shafe makwanni ana zanga-zangar adawa da matakin shugaban kasar Pierre Nkurunziza na neman wa’adin shugabanci na uku.
Akalla masu zanga-zanga 20 suka mutu a arangamar da suka yi da jami’an tsaro a tsawon makwanni biyu da aka shafe ana zanga-zanga. Har yanzu kuma ana ci gaba da zanga-zangar a Bujumbura babbar birnin kasar.
Masu zanga-zangar sun ce matakin Nkurunziza na neman wa’adi na uku ya sabawa kundin tsarin mulki da yarjejeniyar Arusha da ta taimaka aka kawo karshen yakin basasa a kasar.
Majalisar Dinkin Duniya tace kimanin mutane 50,000 suka tsere daga Burundi don fargabar yiyuwar barkewar yakin basasa a kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu