Isa ga babban shafi
Sudan ta Kudu

Masu adawa a da juna a Sudan ta Kudu za su cimma yarjejeniya

Masu adawa tare da yaki da juna a kasar sudan ta Kudu, sun yi shirin gudanar da wata sabuwar yarjejeniyar samar da zaman lafiya a tsakaninsu. yayinda masu sasantawa na Gwamnati, suka bayyana yakinin cewa, za’a samu yarjejeniya mai daurewa tsakanin bangarorin biyu, duk da cewa fada na cigaba da kaurewa tsakaninsu  

Tawagar 'Yan Tawayen Sudan ta kudu a Addis Ababa
Tawagar 'Yan Tawayen Sudan ta kudu a Addis Ababa REUTERS/Tiksa Negeri
Talla

A cewar ministan ‘yada labarai na kasar, kuma jagoran wakilan gwamnati a tattaunawar, Michael Makuei, “mu na da yakinin samar da yarjejeniyar tsagaita buda wuta tsakanin bangarorin kuma zamu halarci taron ne, da nufin maidowa  al-ummar Sudan ta Kudu zaman lafiya”.

Makuei, ya shaidawa manema labarai haka ne, a lokacin da ya ke dab da tafiya birnin Addis Ababa na Ethiopia, inda za’a gudanar da tattaunawar.

Tuni dai wakilan  ‘yan tawayen suka isa Kasar ta Ethiopia domin tattaunawar, yayinda sau bakwai kenan da  suka warware yarjejeniyar tsagaita wuta da suka cimma a baya.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.